Kasar Iran ta sanar da rufe Mashigar Hormuz kwanaki kadan bayan bayyana bude mashigar.

Kasar Iran ta sanar da rufe Mashigar Hormuz kwanaki kadan bayan bayyana bude mashigar.

Tashin hankali a Gabas ta Tsakiya ya sake ƙaruwa bayan Iran ta sanar da rufe muhimmiyar Mashigar Tekun Hormuz, tana mai zargin Amurka da karya yarjejeniyoyi da kuma ci gaba da takura mata.

Iran ta ce matakin da ta ɗauka ya biyo bayan takunkuman da Amurka ke sanyawa jiragen ruwanta, waɗanda ke hana su isa tashoshin su yadda ya kamata.

Mashigar Hormuz dai na da matuƙar muhimmanci ga tattalin arziƙin duniya, domin yawancin man fetur da ake safararsa na ratsa wannan hanya, lamarin da ke sa duk wani cikas a cikinta ke tasiri kai tsaye ga farashin mai a duniya.

Sai dai Shugaban Amurka, Donald Trump, ya bayyana cewa ƙasarsa ba za ta sassauta ba, yana mai cewa za su ci gaba da matsa lamba har sai an cimma sabuwar yarjejeniya da Iran.

A wani ɓangaren kuma, Ministan Harkokin Wajen Iran, Abbas Araghchi, ya yi karin haske cewa duk da rikicin, mashigar na ci gaba da kasancewa a buɗe ga jiragen kasuwanci, inda harkokin zirga-zirga ke gudana cikin tsari.

Kalaman da suka saba wa juna daga bangarorin biyu sun jefa kamfanonin jigilar kaya da masu lura da harkokin duniya cikin ruɗani, yayin da suke ƙoƙarin fahimtar ainihin halin da ake ciki.

A lokaci guda, an samu ɗan sassauci a Lebanon, inda aka kulla yarjejeniyar tsagaita wuta ta kwanaki 10, wadda ta bai wa dubban mutane damar komawa gidajensu bayan tashe-tashen hankula.

Duk da haka, masana na gargadi cewa har yanzu yanayin na da haɗari, inda suke ganin ƙaramin kuskure kaɗai a yankin Tekun Fars na iya haddasa babbar rikici mai faɗaɗa.

Yanzu dai hankula sun karkata kan ko tattaunawar diflomasiyya za ta samar da mafita, ko kuma rikicin zai ƙara tsananta a kwanaki masu zuwa.

Comments

No comments yet. Why don’t you start the discussion?

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *