Janar Oluyede ya bayyana hakan ne yayin ziyarar da ya kai wa sojojin da ke gudanar da aikin Fansan Yamma a Gusau, babban birnin Jihar Zamfara.
Ya ce rundunar tsaro na da ƙudirin kawo ƙarshen matsalar ‘yan bindiga a yankin, inda ya nuna cewa matsa musu lamba akai-akai ne kaɗai zai haifar da dawowar zaman lafiya.
Hafsan ya kuma yaba da rawar da gwamnatin Zamfara da al’ummar jihar ke takawa wajen tallafa wa jami’an tsaro a ƙoƙarinsu na tabbatar da tsaro.

