Kungiyar likitocin Najeriya masu neman kwarewa (NARD) ta bai wa Gwamnati wa’adin kwanaki 21 kan tsaron likitoci.

Kungiyar likitocin Najeriya masu neman kwarewa (NARD) ta bai wa Gwamnati wa’adin kwanaki 21 kan tsaron likitoci.

Ƙungiyar Likitocin Najeriya Masu Neman Ƙwarewa (NARD) ta nuna damuwa kan yadda hare-hare, cin zarafi da tsoratar da ma’aikatan lafiya ke ƙaruwa a sassan ƙasar, inda ta bai wa gwamnatin tarayya wa’adin kwanaki 21 da ta fara aiwatar da matakan kare su.

Ƙungiyar ta bayyana matsayarta ne bayan kammala babban taronta na ƙasa da aka gudanar a Kano, inda ta kuma ayyana rikicin ƙwadago da gwamnati kan wasu muhimman buƙatu da har yanzu ba a warware su ba a fannin kiwon lafiya.

Shugaban NARD, Dakta Mohammad Suleiman, ya ce yawaitar farmaki da cin zarafi kan likitoci na ƙara jefa tsarin kiwon lafiyar Najeriya cikin haɗari, musamman a lokacin da ɓangaren ke fama da ƙarancin ma’aikata da sauran matsaloli.

Ya bayyana lamarin a matsayin babban barazana ga ingancin ayyukan kiwon lafiya da kuma lafiyar ma’aikatan da ke sadaukar da rayuwarsu wajen kula da marasa lafiya.

Daga cikin buƙatun da ƙungiyar ta gabatar akwai gaggauta bincike da hukunta masu kai hare-hare kan ma’aikatan lafiya, ƙara matakan tsaro a asibitoci da cibiyoyin lafiya, da kuma samar da tsarin kariya da martani ga irin waɗannan hare-hare.

NARD ta kuma buƙaci gwamnati ta fara aiwatar da dokoki da tsare-tsaren da za su tabbatar da kare lafiyar ma’aikatan lafiya cikin wa’adin kwanaki 21 da ta bayar.

Ƙungiyar ta yi gargaɗin cewa idan gwamnati ta kasa ɗaukar matakan da suka dace a cikin wa’adin da aka bayar, hakan na iya haifar da ƙarin matakan ƙwadago, ciki har da yiwuwar yajin aiki a faɗin ƙasar.

Comments

No comments yet. Why don’t you start the discussion?

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *