Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) ta Ce ana Amfani da Fyaɗe a Matsayin Makamin Yaƙi a Kasar Sudan.

Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) ta Ce ana Amfani da Fyaɗe a Matsayin Makamin Yaƙi a Kasar Sudan.

 

Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) ta bayyana damuwarta kan yadda ake amfani da fyaɗe da sauran nau’o’in cin zarafin mata ta hanyar lalata a matsayin wani salo na yaƙi a rikicin da ke ci gaba da ƙamari a Sudan.

Babban Kwamishinan Kare Haƙƙin Bil Adama na MDD, Volker Türk, ya ce binciken da ofishinsa ya gudanar ya nuna cewa ana aikata irin waɗannan hare-hare ne saboda dalilai da suka haɗa da ramuwar gayya kan zargin goyon bayan ɓangarorin rikicin, da kuma nuna wariya ta ƙabila.

Ya gargaɗi cewa wasu daga cikin waɗannan laifuka na iya kai matsayin manyan laifukan cin zarafin bil’adama da kuma laifukan yaƙi a ƙarƙashin dokokin ƙasa da ƙasa.

A cewarsa, ofishin MDD ya tabbatar da aukuwar sama da hare-haren cin zarafin mata ta hanyar lalata 500 tun bayan ɓarkewar rikicin Sudan.

Rahoton ya nuna cewa mata da ’yan mata ne suka fi fuskantar waɗannan munanan hare-hare, yayin da ake zargin mayaƙan Rundunar RSF, sojojin Sudan da ƙawayensu, tare da wasu ƙungiyoyin masu ɗauke da makamai, da hannu a yawancin laifukan.

Tun bayan fara rikicin, Sudan na fuskantar matsanancin yanayin jin kai, inda miliyoyin mutane suka rasa matsugunansu, dubban rayuka suka salwanta, yayin da al’ummomi da dama ke ci gaba da rayuwa cikin mawuyacin hali.

Comments

No comments yet. Why don’t you start the discussion?

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *