Da misalin karfe 12:18 na rana agogon Makkah, hasken rana zai ratsa daidai saman Ka’aba, wadda ke zama alkiblar Musulmi a duk duniya.
Masana sun bayyana cewa wannan yanayi na musamman yana bai wa Musulmi da ke kasashe daban-daban damar tantance sahihiyar alkiblar da suke fuskanta yayin gudanar da sallah, musamman idan suka yi amfani da inuwa ko alkibla a wannan lokaci.
Abin lura shi ne, wannan karo na farko cikin shekaru 139 da rana za ta kasance a irin wannan matsayi a ranar Babbar Sallah, ranar da alhazai ke gudanar da muhimman ibadoji kamar Jifan Shaidan, yanka hadaya, aski da kuma Dawafin Hajji.
A lokaci guda kuma, Musulmi mazauna gida a sassan duniya za su kasance suna gudanar da bukukuwan Eidil Kabir da ibadar Layya, wanda ya dace da ranar 10 ga watan Zul-Hijja.
Masana ilimin taurari sun ce wannan al’amari yana faruwa ne saboda yadda duniya ke juyawa tare da tafiyar rana tsakanin yankunan Tropic of Cancer da Tropic of Capricorn.

