Hukumar tace fina finai ta jihar Kano ta dakatar da jaruman kannywood biyu.

Hukumar Tace Fina-finai da daba’i ta Jihar Kano ta dakatar da jaruman Kannywood biyu, Adam Garba da Amina Uba Hassan, daga gudanar da harkokin fim a Jihar Kano har tsawon shekara guda.

wannan na cikin sanarwar da jamiʼin yaɗa labaran hukumar Comrade Abdullahi Sani Sulaiman, ya fitar a madadin shugaban hukumar, Malam Abba El-Mustapha.

Sanarwar ta ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan bayyanar jaruman biyu a wani bidiyo da ta bayyana a matsayin wanda ya saɓa da tarbiyya, lamarin da ya jawo ce-ce-ku-ce a tsakanin al’ummar Jihar Kano.

Hukumar ta bayyana cewa dokar hukumar ta ba ta damar dakatar da duk wani ɗan masana’antar Kannywood daga gudanar da harkokin fim a Kano, tare da gargadin cewa karya dokar na iya jawo hukunci mai tsauri a ƙarƙashin doka.

Shugaban hukumar, Malam Abba El-Mustapha, ya ja hankalin ’yan masana’antar Kannywood da su guji duk wani abu da ka iya zubar musu da mutunci ko taɓa ƙimar masana’antarsu.

 

Comments

No comments yet. Why don’t you start the discussion?

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *