Likitocin Edo sun dakatar da aiki ‘sai an ceto’ mambobinsu da aka sace.
Likitocin Edo sun dakatar da aiki 'sai an ceto' mambobinsu da aka sace.

Likitocin Edo sun dakatar da aiki ‘sai an ceto’ mambobinsu da aka sace.

Likitocin Edo sun dakatar da aiki ‘sai an ceto’ mambobinsu da aka sace.

Ƙungiyar Likitocin Najeriya rashen jihar Edo ta ce sun dakatar da aiki har sai hukumomin ƙasar sun ɗauki matakin kuɓutar da wasu mambobinta biyu da ƴanbindiga suka sace a kan hanyarsu da zuwa wurin aiki a jihar.

Ƙungiyar ta ce ta ɗauki matakin ne domin ganin an kare rayukan duka sauran mambobintu da ke faɗin jihar.

Sakataren ƙungiyar Likitoci ta ƙasar, Dokta Mannir Bature Tsafe ya shaida wa BBC cewa bayan sace likitocin biyu, da aka yi garkuwa da su tare da ɗaya daga cikin ‘ƴan’uwansu, bayanan na cewa an ma kashe ɗan’uwan.

‘’Wannan ne ya ɗaga hankali mambobinmu a matakin ƙasa, musamman waɗanda ake aiki a jihar Edo’’, in ji shi.

Ya ƙara da cewa ƙungiyarsu ta ɗauki matakin sanar da gwamnati halin da ake ciki da kira ga jami’an tsaro don kuɓutar da likitocin biyu.

‘’Don haka muka dakatar da aiki har sai mun ga irin ƙoƙari da hoɓɓasan da jami’an tsaro za su yi don tunkarar matsalar’’, kamar yadda ya yi ƙarin bayani.

Comments

No comments yet. Why don’t you start the discussion?

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *