Karon farko Trump ya amince cewa ƴan ta’adda na kashe Musulmi a Najeriya.

Karon farko Trump ya amince cewa ƴan ta’adda na kashe Musulmi a Najeriya.

TRUMP a karon farko, shugaba Donald Trump na Amurka ya amince cewa ana kashe Musulmai a Najeriya, kodayake ya ce hare-haren da ƴan ta’adda masu iƙirarin addini a ƙasar ta yammacin Afrika ya fi shafar mabiya addinin Kirista.
Da ya ke amsa tambaya yayin wata zantawarsa da kafar New York Times a jiya Alhamis, Trump ya bayyana cewa tabbas ya aminta da cewa hare-haren ƴan bindigar da na ƴan ta’adda a sassan Najeriyar na shafar mabiya addinin Islama.
Kafin yanzu Donald Trump ya ƙi aminta da cewa hare-haren ƴan ta’addan na Najeriya kan shafi mabiya addinin Islama, duk da hujjojin da ke fita kan cewa Musulman ne suka fi rasa rayukansu a hare-haren.
Shugaban na Amurka wanda ya jima yana yiwa Najeriyar barazanar kai mata hare-hare gabanin kai harin na ranar Kirsimati, ya ce muddin aka ci gaba da kisan mabiya addinin Kirista ko shakka babu Amurka za ta ci gaba da kai hare-hare.
A cewar Trump tun farko, bisa buƙatar gwamnatin Najeriya ne Amurka ta ƙaddamar da hari a yankin yammacin Najeriyar mai fama da ayyukan ƴan ta’adda.
Trump ya bayyana cewa gwamnatin Najeriyar ta ƙi amincewa da ɗaukar matakan da suka kamata wajen baiwa Kiristoci kariya a sassan ƙasar.

Comments

No comments yet. Why don’t you start the discussion?

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *